SU WANENE AHLUS-SUNNATI WALJAMA'A NA HAKIKA ?
مؤتمر الدولى : المفهوم الصحيح لأهل السنة والجماعة وأثره في الوقاية من الغلو والتطرف
TAKARDAR BAYAN TARON MALAMAN DUNIYA WANDA YA GUDANA A KASAR KUWAIT, TARON DA YA SAMU HALARTAR MALAMAI DAGA KASASHEN MUSULMAI HAR GUDA ASHIRIN DA BIYAR (25), MALAMAN SUNYI KOKARI MATUKA WAJEN BAYYANAMA DUNIYA SU WANENE AHLUS-SUNNATI WALJAMA'A NA HAKIKA.
ABUBUWANDA SUKA CIMMA MATSAYA AKAI...
1) Ahlus-sunnati waljama'a sune wad'anda suke biyayya ga littafin Allah da Sunnar Manzonsa (SAW), kuma jagororinsu sune Sahabbai sannan Tabi'ai sannan wad'anda suka biyo bayan Tabi'ai sannan wad'anda suka biyo bayansu suma, kuma suka tafi akan Tafarkinsu tareda kyautatawa.
2) Sannan Manhajin Ahlus-sunnati waljama'a guda dayane tilo babu wasu Manhajojin acikinsa.
3) Kuma Gaskiyane karya bata iya tunkudeshi,
4) Sannan Manhajine tsaka-tsaki babu wuce gona da iri acikinsa (Guluwwi).
5) Sannan kuma sabani acikin mas'alolin ijtihadi tsakanin Malaman Mazhabobi hudu (4), Hanafiyya Malikiyya, Shafi'iyya da kuma Hanabila, baya lizimta fita daga Sunna kuma baya halasta kiran mutane da sunaye mabanbanta da jinginasu ga kungiyoyi da gungu-gungu ko kiransu da yan bid'a.
6) Manhajin Ahlus-sunnati waljama'a bai samo asali daga Imam Ahmad bin Hambal ba ko Sheikhul Islam Ibnu Taimiyya ko Sheikhul Islam Muhammad Ibnu Abdulwahhab, abin sani ya samo asaline daga Sahabban Annabi (SAW) Da Tabi'ai da wad'anda suka biyo bayansu.
ALLAH YA FIHIMTAR DAMU YA GASKIYA YA KUMA BAMU IKON BIYAYYA GARETA.
Albany Dabai,
08069123479.
No comments:
Post a Comment
Your Comment will help us to improve