Monday 4 October 2021

DIYAR SHEIKH JAFAR TA ZAMA AMIRA TA NISA'U SUNNAH RESHEN JIHAR KANO.

Tarbiyya Itace Tushen Rayuwa Mai Kyau

Daga Mahmud Isa Yola

Yau a dakin taron kaddamar da shugabanin kungiyar NISA'U SUNNAH reshen jihar Kano, kusan dukkan mahalarta sun zubar da hawayen su a daidai lokacin da 'yar Marigayi Ash-Sheikh Jaafar Mahmud Adam, Malama Zainab Jaafar Mahmud ta ke gabatar da jawabin amincewa da nada ta da kungiyar Izala tayi a matsayar Ameerah. 

Babu shakka ba komai masu kuka suke hararowa ba a wannan lokaci illa mahaifin Malama Zainab. Babu shakka rayuwa mafi albarka, mafi kyau, ita ce wacce aka gina ta akan gaskiya da abunda ta kunsa, kuma kowa zai bada shaida bisa kokarin Marigayi Sheikh Jaafar a wannan bangare. 

A watannin baya, idan baku manta ba wata wasika ta bayyana wacce Sheikh ya rubutowa malama Zainab, a lokacin ya fita kasar Sudan Karatu, inda a ciki yake gaya mata cewa ya samu damar isowa kasar lafiya... A karshen wasikar, shehin malamin yayi mata wasu kalmomi masu tsada inda yace yana mata "wasiyya da jin tsoron Allah a boye da kuma a fili, da yawan tilawar Al-Qur'ani Maigirma, da sallah akan lokaci..."

Wannan shine wasiyyar malam, wanda a dunkule, shine yana so tayi rayuwa mai kyau, wanda zata yi alfahari da shi a ranar gobe. Kuma babu shakka, ďabbaka wannan wasiyya shine yakai malama matsayin da take.

Wannan abun koyi ne ga matasa, kuma izna ne ga iyaye. A daidai wannan lokaci da galibin mutane suka shagaltu da na'urorin sadarwa na zamani, da yawan bin son zuciya da raunin tunani, babu abunda zai komo da martabar rayuwar mu ta zama mai kyau irin wasiyyar malam na cewa mu ji tsoron Allah, mu tsaida sallah, mu yi karatu tare da aiki da Al-Qur'ani.

Allah SWT Ya gafartawa Sheikh. Allah haskaka kabarin sa, Allah karawa zuriyar da ya bari albarka, Amin.

Thursday 17 December 2020

WE ARE AT WAR: LET'S ALL FACE IT BEING THE TEXT OF THE PRESS RELEASE BY ULAMA FORUM ON SECURITY SITUATION IN NORTHERN NIGERIA ON WEDNESDAY JIMADAA ULA 2, 1442H (DECEMBER 16, 2020)

Bismillahir Rahmānir Rahīm.Alhamdu lillah. Wassalātu was Salāmu alā Rasūlillah, wa Ālihi wa Ashābihi wa man wālāh.

It is with a heavy heart that the Ulama Forum makes this press statement, which reflects the deep worries of its members over the deteriorating trend of insecurity in the country, particularly in Northern Nigeria. The Ulama Forum is a collaborative forum of Scholars, Academics, Professionals and leaders of Muslim organizations closely monitoring religious and social issues in the country, communicating, collaborating and conducting extensive researches to unravel Shari'ah rulings and offer advice to all segments of the society, whenever the need arises. 

It can be recalled that the Forum had earlier published a Communiqué on "Security Situation in Northern Nigeria", which was released on June 28, 2020 and shared widely. The statement detailed our humble recommendations to the government, the security agencies, traditional leaders, the Ulama and the public on how to pursue a multi-thronged strategic approach to countering insecurity in the land. We are once again compelled to make another press statement on the same issue, which has gone from bad to worse over the last couple of months.

The Boko Haram insurgency has led to the death of thousands of innocent lives and caused untold hardship to the entire people of the Northeast and Northwest regions. Among the victims were prominent Muslim scholars, traditional, community and political leaders, including an Emir and a retired army General. To worsen an already bad situation, in the last few years, criminals and bandits have entered the scene, pushing the Nation closer to the edge of a cliff. Now, events in the last couple of months have proven the fact that these and several other forces of destruction are desperately trying to push the nation off the cliff and toss us all into a bottomless pit.

Consider the following:
Nov. 9 - 9 students from Nigerian French Language Village, Badagry Lagos were abducted and huge ransom demanded along the Kaduna-Abuja highway in Kaduna State.

Nov. 15 - Another 9 students from Ahmadu Bello University Zaria were kidnapped and N270m ransom demanded along the same Kaduna-Abuja highway in Kaduna State. 

Nov. 17 - The kidnap of 12 police officers on transit to Zamfara from Borno and request for ransom before their release, around Katsina State.

Nov. 18 - Gunmen invaded staff quarters of Nuhu Bamalli Polytechnic and abducted a lecturer and two children in Zaria, Kaduna State. 

Nov. 20 - Gunmen attacked a Juma'at congregation, killed five persons and abducted the Imam and more than 30 others in Dutsen Gari of Maru LGA, Zamfara State. 

Nov 23 - Gunmen invaded a house in the staff quarters of Ahmadu Bello University Zaria and kidnapped a lecturer, while his wife and daughter were rescued after a gun battle with security agents in Zaria, Kaduna State.

Nov 23 - Gunmen kidnapped Agric Minister's brother and demanded ransom in Tofai village, Gabasawa LGA, Kano State.

Nov 29 - The cold-blooded murder of 43 innocent farmers slaughtered on their way to cultivate farm produce in Zabarmari - Borno State. 

Dec 11 - About 400 pupils missing or kidnapped after gunmen stormed secondary school in Kankara, Katsina State.

The Ulama Forum viewed with serious concern the apparent failure of government (at all levels) and the security agencies, to contain the raging insecurity in the region. It noted the growing public disenchantment in the region over the deterioration of security, which has disrupted their activities and made normal life nearly impossible. It is apparent that all the efforts and strategies employed by the government to tackle the insurgency and armed banditry have failed to achieve the desired goal. Something must be fundamentally wrong somewhere and it is absolutely necessary to address the problem squarely. It must be stated without mincing words that the buck lies on the table of the President to do the needful in order to tackle the seemingly intractable problem. 

Members of the Forum observe with all sense of responsibility that unless immediate and decisive actions are taken to halt this dangerous slide into the dark abyss, our beloved country, Nigeria, will collapse sooner than later, creating the worst humanitarian crisis in recent history. We feel highly concerned that despite the continuous assurance that government is winning the war against insurgency, realities on ground point to the contrary.

We are deeply concerned that Boko Haram insurgency, banditry and criminal activities have compounded the challenges of insecurity, leading to wanton loss of innocent lives, kidnapping and abduction of persons, forcing thousands to either flee their homes or live in constant fear and uncertainty, which has led to the collapse of economic and educational activities, creating an astronomical number of orphans and widows that is growing in a frightening and exponential way. 

The Forum observes that, the lack of adequate information from relevant authorities and the clear absence of positive community engagement have created mistrust and dissatisfaction to the extent that apart from physical combat, the Government is currently competing with the Boko Haram murderers in telling the correct position of things.

It further observes that the high levels of poverty, the huge numbers of unemployed youths, the hundreds of thousands of students affected by the seemingly endless ASUU strike, the aftermath of EndSARS protests, coupled with the widespread proliferation of illicit drugs, small arms and dangerous weapons in the country in general, have added fuel to the raging fire of banditry, criminality and destruction.

Similarly, the continued existence of IPOB and similar agents of destruction and national destabilization and the ease with which they mobilize funds and resources for their nefarious activities is another time bomb waiting to explode.  

RECOMMENDATIONS:  
Based on the above, Ulama Forum has resolved as follows:
 1. The Forum most respectfully advises the President, the State Governors and all elected representatives, to sit up to their responsibility and uphold the trust reposed in them - by Allah and then the Nigerian people - to protect the lives, property and honour of Nigerian citizens.

 2. The President should immediately address the nation, declare a State of Emergency on Security in Nigeria, and establish a National Task Force on Security (NTFS). State Governors should also set up a State Task Force on Security (STFS). The NTFS/STFS, which will comprise professionals and security experts, eminent personalities and responsible members of the community to, among other things:

 a. Coordinate and provide complete synergy between all security agencies, monitor and regularly report progress to the President/Governor while updating the public with unclassified information and guidance.  

 b. Collaborate with and between the states in gathering intelligence, mobilizing communities and documenting challenges and progress in the security and peaceful coexistence within and across neighbouring the states.

 c. To identify and track suspicious persons and movements, criminals' hideouts, flashpoints and all sensitive intelligence and notify relevant authorities accordingly. 

 d. Regularly brief the President/Governor and maintain a National/State database of all incidences of security breaches with clearly indicated indices such as location and date of attack, casualties, abductions/kidnappings, response from the security and successes/challenges encountered. 

 e. Whenever there is an attack on a community, immediately coordinate with FEMA/SEMA for emergency response, assessment of the situation and provision of immediate assistance, preparing and submitting comprehensive reports to the President/Governor. 

 f. To identify, track and free abducted and kidnapped persons, facilitate the treatment of the wounded and collaborate with relevant Federal and State Ministries to assist internally displaced persons and provide adequate security for their safe return to their homes.    

 g. Advise the Federal and State governments on measures to monitor and halt the spread of weapons, stimulants and illicit drugs while supporting implementation of government measures against their proliferation across the country. 

 3. Government should take decisive action against deliberate politicization of security and other sensitive matters of national cohesion, deal with the constant attacks at the fabrics that knit us together, quickly and comprehensively resolve the ASUU strike while finding lasting solutions to all the myriads of challenges stated above before the nation collapses.  

In conclusion, the Ulama Forum reiterates the saying of Prophet Muhammad ﷺ that "Whoever wakes up safe in his base, healthy in his body, with enough provision for that day, is like one who was given the world in its entirety", we therefore call upon Government to listen to the cries of its subjects and take drastic measures to protect public peace and security. The President should take full control and should not hesitate to fire any of his lieutenants who fail to perform. 

The Forum urges the President to consult widely with all segments of the Nigerian society with a view to harnessing ideas and informed opinions on the way forward towards ensuring everlasting peace and security in Nigeria. 
Allah says: [Say, "What would my Lord care for you if not for your supplication?"] (Qur'an 25:77). 

Thus, while calling on all to repent and avoid sinful acts, we urge Imams to continue supporting peaceful coexistence, lead their followers in alqunut and intensify prayers for Almighty Allah to bring an end to these challenges, guide our leaders, strengthen them and save Nigeria from the evils of insurgents, tribal separatists, armed bandits, kidnappers and their sponsors may Allah bless Nigeria and its good people.

Alhamdu lillah. Wassalātu was Salāmu alā Rasūlillah.

Signed for and behalf of the underlisted by 
Mal Aminu Inuwa Muhammad (Convener)
Engrr. Basheer Adamu Aliyu (Secretary)

LIST OF PARTICIPANTS

 1. Malam Aminu Inuwa Muhammad, Kano 
 2. Prof. Mansur Ibrahim Sokoto, Sokoto 
 3. Dr. Bashir Aliyu Umar, Kano 
 4. Dr. Abubakar Muhamad Sani B/Kudu, Jigawa 
 5. Dr. Khalid Abubakar Aliyu, Kaduna 
 6. Prof. Muhammad Babangida, Kano 
 7. Prof. Salisu Shehu, Bauchi 
 8. Prof. Ahmad Bello Dogarawa, Kaduna 
 9. Sheikh Abdulwahab Abdallah, Kano 
 10. Sheikh Ibrahim Shehu Maihula, Kano 

 11. Dr. Saidu Ahmad Dukawa, Kano 
 12. Malam Muhammad Lawal Maidoki, Sokoto 
 13. Sheikh Abdullahi Bala Lau, Adamawa
 14. Dr. Ibrahim Adam Omar Disina, Bauchi 
 15. Sheikh Abdulmuttalib A. Muhammad, Yobe 
 16. Barr. Ibrahim Muhammad Attahir, Gombe 
 17. Amir Abdullahi Abubakar Lamido, Gombe 
 18. Sheikh Abba Muhammad Gadanya, Kano 
 19. Sheikh Adam Abdullahi Mohammed, Yobe
 20. Mal Ahmad Bello Aboo Maimoonah, Katsina 
 21. Dr. Muhammad Alhaji Abubakar, Borno 
 22. Malam Aminu Aliyu Gusau, Zamfara
 23. Mal Shehu Muhammad Maishanu, Zamfara
 24. Dr. Ibrahim Abdullahi R/Lemo, Kano
 25. Prof. Muhammad Amin Al-Amin, Katsina 
 26. Dr. Salisu Ismail, Sokoto 
 27. Dr. Muhammad Muslim Ibrahim, Katsina
 28. Dr. Umar Garba Ibrahim (Dokaji), Gombe
 29. Prof. Auwal Ibrahim Magashi, Kano
 30. Dr. Abubakar Saidu, Gombe 
 31. Engr. Ahmad Jumba, Bauchi 
 32. Sheikh Aliyu M. Said Gamawa, Bauchi 
 33. Sheikh Ibrahim Chiroma B/Kudu, Jigawa 
 34. Sheikh Muazu Abba Jabir, Bauchi 
 35. Sheikh Muhammad Sagir Usman, Kano 
 36. Dr Auwal Adam Tilde, Bauchi
 37. Sheikh Yusuf Adam Khalil, Kano
 38. Sheikh Zakariyya Mu'azu, Gombe
 39. Sheikh Idris Yunus, Abuja 
 40. Dr. Usman Jibril Mika'il, Gombe 
 41. Sheikh Aminu Bala, Kano 
 42. Mal Abdul-Rahman Ibrahim Idris, Bauchi 
 43. Engr. Basheer Adamu Aliyu, Jigawa

Saturday 23 May 2020

COMPLETE RAMADAN TAFSEER 1441/2020 Daga Cikin Garin FUNTUA.


Gabatarwa
Sheikh Imam Sa'idu Musa Funtua.

Tare Da:
Alaramma Mal. Ishaq Sulaiman.

Danna link dake kasa domin saukewa a wayarku ku saurara.




 























Ayi sauraro lafiya!

Zaku iya ziyartan wadannan shafukan na Jibwis Social Media Katsina domin samun karatukan malaman sunnah daga ko ina.




Facebook:

©  Nazeer Danjagale
Jibwis Social Media Katsina.
    30 Ramadan, 1441
      23 May, 2020

Wednesday 20 May 2020

JAWABIN RUFE TAFSIRIN RAMADAN NA WANNAN SHEKARA TA 1441/2020 DAGA SHUGABAN KWAMITIN TAFSIR NA KASA KUMA SHUGABAN JIBWIS NA JIHAR KATSINA - Sheikh Yakubu Musa Hassan Katsina

Daga: Yusuf Hassan Buhari

Da sunan Allah Madaukaki wanda dukkan yabo da godiya sun tabbata a gareshi, bisa ni’imominsa masu yawa garemu. Tsira da aminci su kara tabbata ga Annabi Muhammad (S.A.W) wanda aka aiko da littafi wanda 6arna ba ta zuwa gabanshi ko 6ata, tabbatacciyar hanyar tsira daga dukkan duhu zuwa haske. Allah ya kara aminci ga Alayensa da Sahabbansa za6a66u wanda suka yada wannan addini da dukiyoyinsu da rayukansu. Allah kara tabbatar da mu bisa wannan hanya tasu har zuwa ranar sakamako.

Cikin yaddar Allah (SWT) da ba za’a gabatar da Tafsirai ba a cikin wannan Kasa ta mu saboda kalubalen da aka fuskanta na cutar mashako (Covid 19) da ta bayyana cikin duniya baki daya wanda kafin ta shigo wannan Kasa labari mu ke ji, amma kuma kafin watan Ramadan ta fara shigowa wannan Kasa dan haka ne akai matsaya akan dakatar da tura Malamai masu Tafsir da wannan Kungiya ta sa ba gabatarwa duk Shekara ciki da wajen Kasar nan sanadiyyar matakin da aka dauka na hana taruwar mutane a wuri daya wanda ya kun shi kowa wane irin taro wanda ya shafi Tafsirin ba na. Wand aka ba Malamai damar su gabatar da Tafsiransu da shirye-shirye wanda suka shafi wannan wata na Ramadan da kuma wannan hali da ake ciki a Gida tare da Yan Jarida da ‘Yan Social Media domin su isar zuwa ga sauran al’umma
 
Muna addu’a ga Malaman da suka samu dama su ka gabatar da Tafsirai a gidajensu muna rokon Allah yayi masu sakayya ta alkhairi, abubuwan da su kayi wanda yake daidai Allah ya ba su lada wanda kuma ya ke kuskure Allah ya gafarta ma su. Sauran Malamai kuma da ba su samu damar gabatar da Tafsirin ba muna ba su hakuri muna rokon Allah ya cika ma su ladarsu  duk da ba su samu damar da gabatar da Tafsir din ba a wuraren da aka saba turasu ko a garuruwan da suke. Muna rokon Allah yayi masu sakayya da Jannatul Firdausi

Bayan haka, wannan lokaci da muka kasance bisa ni’imar Allah mun fara Tafsirin wannan  majalisi bisa jarabawar da Allah ya saukar garemu na lalurar wannan annoba ta cutar mashako (Covid 19) wanda ta afkowa duniya tare da sanya firgici cikin rayuwar al’umma.

Muna godiya bisa hadin kai da jama’a suka bayar da biyayya akan umurni da aka bi na hukumomi da masana bisa kokarin dakile wannan cuta ta mashako (Covid 19). Muna rokon Allah ya ba mu lada ya kara karemu daga fadawa cikin wannan jarabawa.

Kamar yadda muka fada muku umurnin da wannan Kungiya ta bayar lokacin bude wannan Tafsiri, wanda yau muke kullewa tare da gabatar da wadannan kiraye- kiraye kamar haka:

1. Muna masu jajantawa ga al’ummar wannan Jiha bisa ibtila’in tashe tashen hankula na 6arayin shanu da kasha-kashen da aka rinka aiwatarwa a wasu sassa na wannan Jiha. Muna masu addu’a ga Allah ya jikan wadan da suka rasa rayukansu a wannan ta’addancin haka muna addu’ar Allah ya maida mafi alkhairi ga wadan da suka rasa dukiyoyinsu yayin wannan jarabawa.

2. Kungiya tayi kira ga jama’a tare da neman su taimaka ma jama’a lokacin da aka kulle jama’a a gidajensu bisa kokarin dakile yaduwar wannan cuta. Mun samu hadin kan jama’a tare da raba tallafin abinci ga mutanen Kananan Hukumomin Daura da Dutsinma.

3. Kamar ko wace shekara Kungiya ta na gabatar da kira wajen tallafawa marayu da gajiyayyu, wanda bisa wannan Kungiya ta sabinta Kwamitin Marayu na Jiha tare da tabbatar da yin aiki tukuru wajen ganin aikin Kwamitin ya kara tasiri cikin bayar da tallafi ga marayu tare da inganta tsarin gudanarwa.

Bayan haka muna kira ga al’umma su taimaka da abinda Allah ya hure masu su kai a Masallatan da ke Unguwarsu domin taimakama marayu da gajiyayyu.

4. Muna kira ga jama’a da su cigaba da bada hadin kai wajen bin shawarwari, dokoki da ka’idojin da Malaman lafiya su ke  badawa ga me da samun kariya ga wannan cuta 

5. Haka kuma muna kira ga Hukumomi da Jami’an tsaro wajen yin aiki tukuru domin magance wannan cuta da kuma ta’addancin da ake fama da shi a wannan Jiha ta mu. Muna kira ga wadan da aka daura ma nauyin wannan ayyuka mu samman na samar da tsaro da su dinga sanya ido suna bibiya domin tabbatar da ana aikin. Haka kuma wadan da ake ba tallafi su kaima al’umma na wannan cuta su ma a sanya ido, a tabbatar da tallafin na kaiwa in da ake bukata. Idan Shugabannin suka tsare hakan su ma Allah zai tsare su.

Daga karshe muna kara ba da hakuri ga yan’uwa bisa rashin tura Malamai ma su Tafsir da akai a wannan Shekara saboda yana yin da muka tsinci kan mu ciki. Su ma Manyan Maluman da aka saba turawa ciki da wajen Kasar nan domin zuwa gabatar da Tafsir muna ba su hakuri bisa rashin samun gabatar da Tafsir sakamakon halin da ake ciki.

Muna rokon Allah ya ansa mana ayyukanmu  da mu kayi a cikin wannan wata na Ramadan ya kuma yi mana baiwa da samun lada akan ayyukan da mu keyi wannan karon ba mu samu damar yi ba. Allah yayi mana jagora yaba mu zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Wassalamu Alaikum Wa Rahamatullahi Wa Barakatuhu

Naku a Musulunci
Sheikh Yakubu Musa Hassan
Shugaban Kwamitin Tafsir na Kasa 
Shugaban JIBWIS na Jihar Katsina
27 Ramadan, 1441
      20 May, 2020

Tuesday 5 May 2020

SAKON TA'AZIYYA GA YAN'UWA DA IYALAI. DAGA SHUGABAN JIBWIS NA JIHAR KATSINA

SAKON TA'AZIYYA GA YAN'UWA DA IYALAI

Shugaban JIBWIS na Jihar Katsina  Sheikh Yakubu Musa Hassan Katsina ya mika sakon ta'aziyya ga iyalai da yan'uwa da sauran al'umar musulmai bisa rashe rashen yan'uwa da ake tayi a kwanakin nan

Shugaban ya mika sakon ta'aziyya ga iyalan:

Alh. Malami Usman Ma'aji
(Ma'ajin Kungiyar JIBWIS reshen Jihar Sokoto)
Wanda Allah yayi ma rasuwa ranar 4-9-1441/ 26-4-2020

Alh. Abdulkadir Adamu Jega 
Mai Ladabtarwar Majalisar Agaji ta Kasa, (National Discipline Officer FAG of JIBWIS) 
Wanda yayi ma rasuwa ranar Lahadin da ta gabata

Amb. Dr. Tafida Abubakar Ila Autan Bawo
(Sarkin Rano)
Wanda Allah yayi ma rasuwa ranar Asabar din da ta gabata 2-5-2020

Alhaji Muhammad Ahmad Asha
(Sarkin Kauran Namoda)
Wanda Allah yayi ma rasuwa ranar Lahadin da ta gabata 3-5-2020

Alhaji Iro Sabe
(Kilishin Katsina)
Wanda Allah yayi ma rasuwa yau Talata 5-5-2020

Alhaji Faruk Lawal Bakiyawa
Wanda yan ta'adda suka shiga gidanshi suka kasheshi a daren yau Talata a Garin Bakiyawa

Haka kuma ya na meka sakon ta'aziyyar  ga sauran yan'uwa wadan da suka rasa makusantansu a fadin Jihar Katsina da ma Kasa baki daya

Shugaban JIBWIS Sheikh Sautus Sunnah, ya gabatar da sakon ta'aziyyar ne ga 'yan uwa da iyalan mamatan a Madadin Kungiyar JIBWIS ta Jihar Katsina da yammacin yau Talata yayin da yake gabatar da Tafsirin Ramadan na yau


Muna rokon Allah Ubangiji ya baiwa iyalansu hakuri, ya jikansu, ya gafarta masu, yasa mutuwa hutuce a garesu, tare da sauran wadanda suka rigaye mu, cikin musulmai muminai. Wadan da wannan annoba ta zama silar ajalinsu Allah ya kar6i shahadarsu

Daga karshe yayi addu'ar Allah ya kwaranye mana wannan annoba da ta addabi duniya, ya kawo mana karshenta. Ameen

Yusuf Hassan Buhari
     JIBWIS Katsina
  12 Ramadan, 1441
        5 May, 2020

Friday 24 April 2020

ANYI KIRA GA 'YAN SOCIAL MEDIA DA SU KIYAYE: HARSHEN SU, HANNUWAN SU DA IDANUWAN SU


A KODA YAUSHE, ALOKACIN DA SUKE DUBA WAYAR HANNUN SU.

Daga: Shehu A.A.Gashua
          Via
Ibrahim Baba Suleiman

 Harshe yana da Tasiri kwarai da gaske , illa iyaka mu kiyaye shi yayin furta magana mai kyau ko maras kyau.

  Mu guji muggan maganganu a lokacin rubutun ta wannan kafa akan Malamai,Shugabannin mulki da sauran Abokan Aikin mu.

 Mu daina cin mutuncin mutane sakamakon rashin jituwar mu da su na Banbancin Siyasa,Bangaren Addini,Bangaren kungiyoyin mu da sauran su.

  Kada mu yarda hannuwan mu su rubuta karya,kazafi,munafurci da sauran su. Mu tuna fa lalle ne muna tare da mala'ikun Allah masu daukar dukkan lamuran mu masu kyau ko akasin hakan.

 Lalle ne muyi hattara da hotun batsa dake cikin wannan kafa dake shugomana ba tare da sanin mu ba. Idanuwan mu kada su kasance masu leke leken banza domin ganin mugun abu.

 Allahu Akhbar, Allah ya shigo damu cikin watan Ramadan, wata mai Albarka watan da Allah yake ninka ladan Ayyukan bayin sa. Lalle mu kasance masu Rubuta,fadin,ganin Alkhairi a lokutan Ayyukan mu ta wannan kafa.

 Mu kasance musu biyayya da taka tsantsan a koda yaushe wajen bin dokokin wannan Aikin na Social Media. Allah ya yi mana Jagora.

Naku: Shehu A. Abdurrahman Gashua
National photo Editor
Jibwis Social media Nigeria

Sunday 19 April 2020

BEING A COMMUNIQUE ISSUED AT END OF MEETING HELD ONLINE BY JIBWIS SOCIAL MEDIA NATIONAL EXCOS.


23 SHA'ABAN, 1441(17/4/2020).

*The national exco symphatize with People world and Nigeria in specific, especially the Muslim Ummah with regard to the current situation of COVID19 PANDEMIC.*

The  meeting after a series of deliberations brought forward the following resolutions:

*1. The meeting has considered the CURRENT SITUATION ON COVID-19 and resolved to follow the order from the National Chairman of JIBWIS Sheikh Dr. Abdullahi Bala Lau on online posting of daily Tafaseer by different scholars across the country,*

*2.  The meeting has also agreed to come up with a stirring committee to coordinates and communicate as urgent to state branches the use of appropriate app that can suit the activities. As it may be live streaming app, live video app, audio note app and etc*

*3. The meeting resolved that, as directed by Dr. Sheikh Abdullahi Bala Lau all state exco of JIBWIS should provide the Social Media men with an incentive that will relief the burden of buying internet data for the period of Ramadan fasting*

*4. Following the deliberations on the need for a concerted daawah activity within  & outside Nigeria and procurement of working materials & mobilization resource personnels, the meeting emphasized on the need to mark out plans and strategies of having a tangible & sustainable source of income for the movement*

*5.  The meeting was finally adjourned*

     Gaddafi Shehu
 Deputy National Sec. Gen. 
*JIBWIS NEW MEDIA*

24 SHA'ABAN 1441 (18/4/2020)