Tuesday, 6 December 2016

LABARAI A TAKAICE


*Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya gana da shugabar Laberiya Mrs. Ellen Johnson Sirleaf kan lamuran tsaron yankin Afurka ta yamma.

*Ganawar dai tazo ne gabanin taron lamuran tsaro da zaman lafiya na birnin Dakar din kasar Senegal.

*Laberiya dai na daga kasashen Afurka ta yamma da su ka dandana kudar yakin basasa inda hakan ya yi sanadiyyar zubar da jini har ma ga tsohon shugaban kasar Samuel Doe.

*Najeriya dai ta tallafa wajen dawo da zaman lafiya a Laberiya ta hanyar kafa rundunar taron dangi ta "ECOMOG" da Janar Timothy Shelpidi mai ritaya ya jagoranta.

*Shugabanni a yankin Afurka da manyan jami'ai sun taru a babban birnin Senegal, Dakar don taron wanzar da zaman lafiya da tsaro.

*Taron dai wanda zai kammala a talatar nan,zai samu karfin guiwar cimma muradu daga kungiyar Afurka AU.

*Shugaban Senegal Macky Sall ne ke jagorantar taron.

*Wassu abubuwan da a ke saran taron zai tabo akwai 'yancin dan adam da lamuran jinkai.

*Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya soki majalisar dinkin duniya da sauran kungiyoyin bayar da agaji saboda "zuzuta" halin da 'yan gudun hijirar da Boko Hara suka kora daga gidajensu ke ciki.

*A wata sanarwa da kakakin shugaban kasar Malam Garba Shehu ya fitar, ya ce kungiyoyin suna kambama halin da 'yan gudun hijirar ke ciki ne da zummar samun kudi daga wajen gwamnatoci.

*Ya bayar da sanarwar ce kwanaki kadan bayan majalisar ta dinkin duniya ta ce fiye da mutum 5m da Boko Haram ta raba da muhallansu na fuskantar hatsarin kamuwa da mummunar yunwa.

*Ku gaggauta Gamawa Da 'Yan Boko Haram, Domin Ina So Na Mayar Da Ku Bariki A Shekarar 2017, Sakon Janar Buratai Ga Sojojin Naijeriya

*Gwamnatin jihar Kaduna tace kungiyar Shi'a kungiya ce da ayyukanta gaba daya ya jibinci nuna tawaye ga dokokin kasa saboda haka daga yau ta ajiye ta a matsayin kungiyar yan tawaye.

*Gwamnatin ta ce shugaban 'yan kungiyar Ibrahim El-Zakzaky da yake kulle a yanzu haka, shine za a' dora ma alhakin duk laifukan da mabiya akidar Shi'a din suka aikata domin shine jagoransu.

*Gwamnatin Naijeriya zata haramta shigo da motoci ta iyakokin kasa kamar yadda kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN ya rawaito.
Duk wata mota da za a shigo da ita yanzu, sai dai ta ruwa.

*Wanda duk zai shigo da mota ta iyakokin kasa, zai iya yin hakan nan da zuwa 31 ga Disambar 2016." Inji Adeniyi. 

*Wannan dai yana zuwa ne a lokacin da gwamnatin ta haramta shigo da shinkafa ta iyakokin kasa tun a afrilun 2016. Abin da ya jawo ta yi tashin gwauron zabi.

Ibrahim Baba Suleiman
Jibwis Social Media
06/Rabi-Al'Awwal/1438
06/December/2016

No comments:

Post a Comment

Your Comment will help us to improve