Monday, 5 December 2016

LABARAI A TAKAICE


*Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari zai sauka a birnin Dakar din kasar Senegal don taron zaman lafiya da tsaro karo na uku na "DAKAR"

*Shugaban Senegal Macky Sall ne zai jagoranci taron.

*Taron dai wanda na kwana biyu ne daga litinin din nan, zai samu bayanai na bunkasa tsaro daga kungiyar hadin kan Afurka AU.

*Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce ba daidai ba ne kalaman da mai martaba sarkin Kano Muhammadu Sanusi II ya yi cewa gwamnatinsa ta karbi N4.5tr, yana mai cewa N1.5tr ta karba.

*A wata sanarwa da kakakin shugaban kasar Malam Garba Shehu ya fitar, yace ya kamata mai martaba ya tsaya a matsayin sa na Sarki

*Tsofaffin shugabannin hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin Najeriya ta'annati, EFCC, Nuhu Ribadu da Farida waziri sun zargi juna da hannu wajen aikata cin hanci da rashawa.

*Wata sanarwa da Farida Waziri ta fitar ta ce ya kamata Malam Nuhu ya yi wa 'yan Najeriya bayani kan biliyoyin kudi da kadarorin da ya kwace daga wurin mutanen da ake zargi da cin hanci lokacin da yake shugabanci hukumar.

*Tana mayar da martani ne kan zargin da Nuhu Ribadu ya yi mata a makon jiya cewa tana cikin mutanen da suka hana ruwa gudu a fafutikar da ya yi ta hukunta mutanen da ake zargi da cin hanci a kasar.

*Tsofaffin manyan jami'an EFCC din dai ba sa jituwa da juna tun bayan da aka maye gurbin Nuhu Ribadu da Farida Waziri a hukumar ta EFCC, matakin da a wancan lokacin, 'yan kasar da dama ke yi wa kallo na yunkurin hana Ribadu hukunta wasu shafaffu da mai.

Ibrahim Baba Suleiman
Jibwis Social Media
05/Rabi-Al'Awwal/1438
05/December/2016

No comments:

Post a Comment

Your Comment will help us to improve