*Cin Hanci Da Rashawa Ne Silar Fadawar Nijeriya Cikin Mawuyancin Hali, Inji Shugaban Hukumar EFCC, Ibrahim Magu
*Za Mu Marawa Hukumar EFCC Baya Domin Yakar Cin Hanci Da Rashawa, Inji Rundunar Sojin Naijeriya
*Rundunar ta bayyana hakan ne a yayin da shugaban hukumar EFCC, Ibrahim Magu ya kai mata ziyara a hedikwatar ta dake Abuja a jiya Juma'a.
*Tsohon shugaban hukumar EFCC Nuhu Ribadu ya ce Farida Waziri na daga cikin wadanda suka yi ruwa sukai tsaki wajen ganin hukumar ba ta cimma burinta ba na ganin duk wanda ya ta ba kudin gwamnati ya dawo dashi.
*Ribadu Ya ce tsohon ministan Shari'a Micheal Aaondoka, da Mai shari'a Ben Nwabueze suma suna gaba gaba wajen ganin ba'a samu nasara ba duk da kokarin da hukumar tayi a wancan lokacin.
*Bai Kamata A Sanya Ido Kan Kayan Lefena Ba, Inji 'yar Shugaban Naijeriya Zahra Buhari
*Shugaban Kasar Gambia, Yahya Jammeh Ya Fadi Zabe Bayan Ya Yi Shekaru 22 A Kan karagar Mulki
*Yahya Jammeh ya fadi zaben shugabancin kasar ne, inda abokin hamayyarsa Adama Barrow ya doke shi.
*Mista Barrow ya samu kuri'u dubu 263,515, yayin da shi kuma Jammeh ya samu kuri'u dubu 212,099, kamar yadda hukumar zaben kasar ta bayyana.
*Shugaban na Gambia, Adama Barrow wanda aka haifa A Adama Barrow a shekarar 1965 a wani kauye da ke kusa da garin kasuwancin nan na Basse a gabashin Gambia, kuma ya zauna a birnin London a matsayin mai jiran kanti.
Ibrahim Baba Suleiman
Jibwis Social Media
03/Rabi-Al'Awwal/1438
03/December/2016
No comments:
Post a Comment
Your Comment will help us to improve