*Manyan malaman musulunci sun taru a babban birnin Najeriya Abuja inda su ka fara gabatar da darussan kyakkyawar akida ga musulmi.
*An ga musulmi maza da mata a taron na wuni biyu da ke gudana a babban dakin taro na kasa da kasa "international conference centre" Abuja.
*Taron dai na gudana a rikunoni daban-daban a duk dakunan taron. Baya ga manyan malaman Ahlussunnah wal jama'a na Najeriya da su ka hada da Sheikh Tajuddeen Adegun, Sheikh Dr. Isa Ali Pantami da Abubakar Sadeeq na masallacin Annur, an samu bakin malamai da su ka hada da Mufti Menk, Sheikh Assim Alhakim da Sheikh Sa'eed Rageh daga kasar Kanada.
*Mahalarta taron kan samu damar yin tambayoyi inda malaman ke amsawa bisa hujjoji masu inganci.
*Mai martaba sarkin Kano Alhaji Muhammadu Sanusi II ya ce kuskure ne gwamnatin Naijeriya tace za ta ciwo bashin kusan dala biliyan talatin, akan cewa za ta biya bashin a cikin shekaru biyu.
*Da yake jawabi a wajen wani taro a Abuja, Sarki Sanusi ya ce ciwo bashin, abu ne mai kyau, amma idan har gwamnatin za ta samu sassauci a yarjejeniyar bashin, sannan kuma a yi amfani da kudin wajen bunkasa bangaren makamashi, da lantarki da gina hanyoyi.
*Shugaban Naijeriya, Muhammadu Buhari ya taya zababben Shugaban kasar Gambiya, Adama Barrow murnar lashe zabe sannan kuma ya yaba wa Shugaba Mai barin Gado bisa dattakon da ya nuna na amincewa da sakamakon zaben.
*A nasa bangare, Shugaban kasar Gambia mai jiran gado, Adama Barrow, ya ce, idan har akwai yiwuwar gurfanar da shugaban kasar mai barin gado, Yahya Jammeh, to za a bi ka'ida wajen hakan.
*Adama Barrow ne dai ya kayar da Yahya Jammeh da tazarar kuri'a fiye da 50,000.
Mutane suna ta yin kira da a gurfanar da Yahya Jammeh bisa ayyukan take hakkin jama'a da ake zargin ya aikata.
*Anga wani faifan Video da ya nuna Shugaban Kasar na Gambiya mai barin gado, Yahya Jamme a lokacin da ya buga waya yana taya abokin takararsa, Adama Barrow murnar lashe zaben kujerar shugabancin kasa da yayi kamar yadda Shugaba Jonathan ya yi a zaben 2015 inda ya buga wa Shugaba Buhari ya taya shi murnar lashe zaben.
Ibrahim Baba Suleiman
Jibwis Social Media
04/Rabi-Al'Awwal/1438
04/December/2016
No comments:
Post a Comment
Your Comment will help us to improve