Friday, 2 December 2016

LABARAI A TAKAICE


*Gwamnan jihar Yobe, Ibrahim Geidam a jiya Alhamis ya tallafa keyar daya daga cikin kwamishinonin sa zuwa gida sakamakon kama shi da laifin kwarara barci har da munshari a lokacin da gwamnan yake gabatar da kasafin kudi na bana a gaban majalisar dokokin jihar.

*Rahotanni sun nuna cewa kwamishinan ya fara sharara barcin ne a daidai lokacin da gwamnan yake karanto jawabai kan kasafin kudin.

*Kimanin Naira Tiriliyan 7.2 Aka Ware Don Kasafin 2017
Ministan kasafi da tsare-tsare Udoma Udoma, shi ya shaida hakan ga manema labarai.

*Mutane 5000 ne yan gudun hijira a sansanoni dabam dam da ke jihar Borno suke dauke da cutar Kanjamau wato HIV.

*Kamar yadda wani malamin lafiya, Hassan Mustapha ya sanar ma kamfanin Dillancin Labarai, ya ce sama da 1000 daga cikin masu dauke da cutan suna sansanin gdun hijiranne da ke Bama, 3000 kuma suna Gwoza.

*Ya ce mafi yawa daga cikin masu dauke da cutan ba sa so asani. sannan kuma ya koka da yadda gwamnati bata ba su cikakken kula.

*Farfesa Wole Soyinka ya ce ya cika alkawarin lalata katin shaidar sa ta zaman Amurka kamar yadda ya yi alkawari matukar Donald Trump ya lashe zaben kasar.

*Kasar Gambia da ke yankin Afurka ta yamma na gudanar da zaben shugaban kasa inda shugaba Yahaya Jameh ke fuskantar adawar wani dan kasuwar gidaje Adama Barrow.

*Kasar dai da ke iyaka daya da Senegal ta kashe layukan buga waya ketare da na yanar gizo don lamuran zaben.

*Jameh dai ya ce Allah zai ba shi damar lashe zabe a karo na biyar.

*Adama Barrow na da farin jini tsakanin 'yan adawa.
Kasar Ghana ma za ta gudanar da babban zabe a ranar 7 ga watan nan.

Ibrahim Baba Suleiman
Jibwis Social Media
02/Rabi-Al'Awwal/1438
03/December/2016

No comments:

Post a Comment

Your Comment will help us to improve