Thursday, 1 December 2016

LABARAI A TAKAICE


*Dakatar da umurnin kara farashin sayan damar shiga yanar gizo da hukumar kula da kafafen sadarwar Najeriya NCC ta yi, ya kawo ajiyar zuciya ga wadanda na zanta da su.

*Tun farko dai NCC ta umurci manyan kamfanonin sadarwar da ke samarda damar shiga yanar gizo baya ga aika yan gajerun sakonni da buga waya,su kara farashin sayar da maaunin shiga  yanar DATA don ba wa kananan kamfanoni damar cin riba a kasuwar sadarwar Najeriya.

*Shugaban ma'aikatar kula da karban haraji na kasa, 'Federal Inland Revenue Service FIRS' Tunde Fowler ya ce daga yanzu mai neman fasfo din kasar Najeriya sai ya nuna takardar shidan biyan haraji kafin ayi masa fasfo.

*Fowler ya fadi hakan ne ranar Litinin a wani taro da ya gudana a garin Abuja.

*Ya yabi jihar Kano da Legas akan kokarin da sukeyi wajen inganta tara haraji a jihohinsu.

*Shugaban Rundunar Sojan kasa, Janar Tukar Burutai ya bayyana cewa dukkan manyan hafsoshin soja za su tafi Maiduguri don gudanar da bukukuwan Kirismeti da na sabuwar shekara tare da sojojin da ke yaki da Boko Haram.

*Ya kuma tabbatar da cewa sojojin sun fara kutsawa cikin kukurmin dajin Sambisa wanda nan maboya ta karshe na mayakan Boko Haram wanda a cewarsa, wannan shi ne mataki na karshe na murkushe mayakan tare da kwato mutanen da suka yi garkuwa da su

*A zaman jiya Laraba ne Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Abubakar Bukola Saraki ya karanto wasikar da Mista Omogunwa, Sanata mai wakiltar shiyyar Jihar Ondo ta Kudu ya aikawa majalisar na sanar da ficewarsa daga PDP zuwa APC.

*Tun kafin zaben gwamnan jihar da aka yi a ran Asabar da ta wuce, a dalilin rabuwar kai a PDP.

*Daga nan sai shugaban marasa rinjaye na majalisar, Sanata Godswill Akpabio ya mayar da martani da cewar babu wata rabuwar kai a PDP, wannan ya haifar da hayaniya a majalisar tsakanin sanatocin PDP da na APC wanda suke yi wa sabon sanatan maraba.

*Daga nan sai sanatocin PDP karkashin jagorancin Sanata Akpabio suka fice daga zaman majalisar

*Majalisar Dokokin Nijeriya na kokarin yin doka da za ta rage yawan shekarun masu iya tsayawa takara saboda matasa su samu damar taka rawa a harkokin gudanar da Nijeriya.

*Dokar a yanzu haka ta samu karatu na biyu a majalisar dokokin, dokar na neman a rage shekarun mai tsayawa takarar shugaban kasa daga shekaru arba'in, zuwa talatin, na kujeran Gwamna kuma daga shekaru talatin da biyar zuwa talatin, na 'yan majalisar tarayya dana jihohi a rage daga shekaru dalati zuwa ashirin da biyar.

*Binciken da wassu kwararru na duniya su ka gudanar ya gano wani bututun aika makamai da Iran ta shunfuda da ke samawa 'yan tawayen Shi'a na Houthi makamai.

*Bututun dai na shunfude ne daga Iran ya bi ta Somaliya zuwa Yaman.

*Iran dai ta sha musanta taimakawa 'yan tawayen Yaman 'yan Shi'a da ke yakar halattacciyar gwamnatin kasar ta Abed Rabbo Mansur Hadi.

Ibrahim Baba Suleiman
Jibwis Social Media 
01/Rabi-Al'Awwal/1438
01/December/2016

No comments:

Post a Comment

Your Comment will help us to improve