*Hafsan Hafsoshin sojojin kasan Najeriya Laftanar Janar Yusuf Buratai ya ce dakarun sojan Najeriya na dannawa cikin dajin Sambisa don rugurguza tungar 'yan Boko Haram.
*Buratai da ke magana a Abuja wajen wani taro yabawa yunkurin sojoji,ya ce wannan yunkuri na da zummar kakkabe burbudin 'yan Boko Haram da ke makale a dajin.
*Dama an samu kwato duk garuruwan da a da Boko Haram su ka kwace da kafa haramtacciyar daular 'yan ta'adda masu zubar da jinin al'umma ba bisa ka'idar kowacce shari'a ba.
*Majalisar dokokin jihar Katsina ta kafa wani kwamiti wanda zai bincike zargi zargen da ake yi na karuwar ayyukan luwadi da madigo a tsakanin daliban da ke makarantun kwana a duk fadin jihar.
*Haka ma, majalisar za ta fadada binciken a kan kwalejin kimiyya da fasaha ta Hassan Usman Katsina mallakar gwamnatin jihar inda majalisar ta kuma tsara bullo da wani shiri na wayar da kan dalibai kan illar dabi'ar Luwadi da madigo.
*Majalisar tarayya ta amincewa Shugaban. Kasa, Muhammad Buhari kan bukatar da ya gabatar majalisar na neman yin Sauyi a kasafin kudin 2016 ta yadda zai karkatar da wasu kudi da aka tanada tun farko don shirin tallafi na musamman zuwa wajen manyan ayyuka.
*A makon da ya gabata ne majalisar ta ki amincewa da bukatar bisa hujjar cewa Shugaban bai bi hanyar da ta dace ba wajen gabatar da bukatar. Sai dai kuma majalisar ta yi karin Naira Bilyan 33 daga bukatar shugaban na shirin yin amfani da Naira Bilyan 180 daga cikin Bilyan 500 da aka ware don shirin tallafawa marasa galihu.
Ibrahim Baba Suleiman
Jibwis Social Media
01/Rabi-Al Awwal/1438
30/November/2016
No comments:
Post a Comment
Your Comment will help us to improve