*Shugaban kungiyar JIBWIS Imam Abdullahi Bala Lau ya nuna matukar mamakin wani faifan bidiyo da a ke yayatawa a kafar labarun yanar gizo cewa ya tura Sheikh Hussaini Zakariyya zuwa wajen Sheikh Dahiru Bauchi ya ba shi hakuri da ma nuna shehin na darikar tijjaniyya tamkar uba ya ke a gare shi.
*Imam Bala Lau ya ce sam bai aiki kowa ya je ba da hakuri a kan laifin da bai ma san menene ba ne in ka debe wa'azin da kungiyar ta ke yi na kira tsaida SUNNAH DA TURE BIDI'A.
*Sanarwar da ta fito ta kafafen yanar gizo na "JIBWIS NIGERIA" na nuna ko ma da Imam Bala Lau zai aika wata tawaga to da zai zama cikin daya daga jami'an ofishin sa ko daya daga shugabannin kungiyar na Izala kama daga matakin tarayya, jihohi har zuwa kananan hukumomi.
*Shehin malamin ya ce kungiyar JIBWIS ba za ta daina yaki da bidi'o'I ba har abada.
*Faifan bidiyon dai ya nuna Sheikh Hussaini Zakriyya wanda mai tafsiri ne a masallacin Othman Ben Affan a Abuja da wassu malaman da su ka hada da na darika har ma da jami'ar asusun BIL GATES a Najeriya Dr. Mairo Mandara.
*Da alamu wannan tawaga ta malamai ne da likitoci masu wayar da kan al'umma kan cutar shan inna da sauran su amma ba tafiyar kungiyar JIBWIS BA CE
*Kwamitin amintattu na jam'iyyar adawa ta PDM a Najeriya ya tsige shugaban jam'iyyar Bashir Ibrahim Yusuf daga mukamin sa da zargin aikata laifuka da barin jam'iyyar ta zama kara zube.
*Jam'iyyar a taron ta a Abuja ta nada kwamitin riko karkashin Munir Garba Waziri da zai yi aiki tsawon wata 3 gabanin sabon zaben sabbin shugabanni.
*Da yake maida martani, Bashir Yusuf yayi watsi da tsigewar da zargin wani babban dan siyasa ne ya iza wutar don samun madafar tsayawa takarar shugaban kasa a 2019.
*Yusuf ya ce da an bi ta lalama da zai iya sarayar da mukamin na sa amma tun da an nuna abun da ya fassara da karfi,ya ce a zuba a ga wanda ke da gaskiya.
*Dan takarar jam'iyyar PDP a zaben gwamnan Ondo ranar asabar din nan 26 ga wata, Eyitayo Jegede ya bukaci hukumar zabe ta dage zaben da tsawon kwana 30.
*Jegede wanda ya samu nasarar takarar a kotu da maye gurbin Jimoh Ibrahim,ya ce dage zaben zai ba shi damar mika wakilan da za su kula ma sa da kuri'u.
*Dan takarar ya nuna kara wa'adin ne zai dace da dokar zabe.
*Shugaban kwamitin amintattun PDP Sanata Walid Jibrin ya yabawa kotu da ta ba wadan takarar nasara ya na mai cewa zai lashe zaben gwamnan Ondo….
*A bangaren ta jam'iyya mai mulki a Najeriya APC na mara baya ga dan takarar ta Ekeredelu don samun nasarar lashe kujerar gwamnan.
*Duk da uban jam'iyyar Sanata Bola Ahmed Tinibu ba ya mara baya ga dan takarar da sa kafar wando daya da shugaban jam'iyyar John Oyegun; hakan bai hana shugaban Najeriya Muhammadu Buhari tattaki zuwa birnin Akure ba inda ya daga hannun Ekeredelu da yi ma sa fatar samun nasara.
Ibrahim Baba Suleiman
JIBWIS Social Media
25/Safar/1438
25/November/2016
No comments:
Post a Comment
Your Comment will help us to improve