Thursday, 24 November 2016

LABARAI A TAKAICE


*Kotun daukaka ta Najeriya ta ayyana dan takarar bangaren Makarfi na jam'iyyar PDP a Eyitayo Jegede a matsayin sahihin dan takarar jam'iyyar a zaben gwamnan jihar Ondo wanda za'ayi ranar asabar din nan mai zuwa 26 ga wata.

*Wannan hukuncin dai ya ture takarar Jimoh Ibrahim na bangaren PDP karksahin sanata Ali Modu Sherif.

*Yanzu dai za a jira a ga yadda hukumar zabe za ta sauya sunan Jimoh Ibrahim da na Jegde don zaben.

*Kazalika bangaren Ali Sherif na da hurumin daukaka kara zuwa kotun koli.

*Shugaban Kasa Muhammad Buhari ya ba Ministan Ilimi, Malam Adamu Adamu umarnin haramta koyarwa ga duk wani malamin da ba ya da kwarewa da kuma wadanda ba su yi rajista ta hukumar yi wa malamai rajista ta kasa ( TRCN).

*Da yake karin haske kan haramcin, Ministan Ilimi, Adamu ya ce duk wanda bai da rajista da hukumar TRCN ba zai samu cin gajiyar shirin gwamnati na daukar malamai 500,000 da aka fara yi a yanzu ba inda ya kalubalanci duk wani Malami da bai yi rajista ba da ya gaggauta yin hakan.

*Tunda Buhari Ya San Cewa An Zabe Shi Ne Domin Kawo Canji A Kasar Nan, To Ya Kamata Ya Daina Duba Kura-kuran Da Shugabannin Baya Suka Yi, Ya Yi Kokarin Mayar Da Hankali Kan Yadda Za A Shawo Kan Matsalolin Kasar Nan, Inji Tsohon Shugaban Naijeriya  Obasanjo

*Babban Sufeton 'yan sandan Najeriya ya ce jami'ansa 128 ne suka mutu sakamakon hare-haren da masu tsattsauran ra'ayi suka kai musu a bakin-aikinsu.

*Wata sanarwa da kakakin rundunar 'yan sandan kasar DCP Don N Awunah ya aike wa manema labarai ta ce an kashe jami'an 'yan sandan ne a sassa daban-daban cikin wata uku.

*Hukumomi a jihar Zamfara sun ce an saki mutane sama da 40 da masu fashin shanu suka sace a farkon a makon jiya.

*Tsohon shugaban Naijeriya Oludegun Obasanjo ya ce abin kunya ne a ce wai duka 'yan majalisar wakilai su taru akan Abdulmumini Jibrin mai makon su duba abinda yake kira akai ne domin a gyara irin tabargazan da ake tafkawa a majalisar.

*Obasanjo Yace Abdulmumini Jibrin ya na da gaskiya akan abubuwan da yake fadi amma maimakon su bi hakan domin a gyara sai gaba dayansu suka taru masa akai domin wulakantashi saboda basu da gaskiya.

*Kakakin majalisar wakilai Yakubu Dogara ya nuna fushinsa akan yadda jami'an hukumar tsaro na sirri wato SSS suka far ma gidajen wadansu alkalai domin bincikansu akan zargin cin hanci da ake musu.

*Kakakin majalisar ya fadi hakanne yau lokacin da ya ke kaddamar da wata kwamiti da ya kafa domin binciken ayyukan hukumar SSS din.

*Ya ce abinda hukumar SSS ta keyi yanzu bai da ce ba saboda ta na irin aikin hukumar EFCC ne.

*Shi kuwa tsohon shugaban Najeriya Olusegun Obasanjo cewa yayi abinda gwamnatin Buhari take yi domin tsaftace fannin shari'a na kasa yayi dai-dai soboda irin lalacewan da fannin tayi.

Ibrahim Baba Suleiman
Jibwis Social Media
24/Safar/1438
24/November/2016

Sent from my Windows Phone

No comments:

Post a Comment

Your Comment will help us to improve