*Hukumar zaben Najeriya ta ce ta kammala shirin gudanar da zaben gwamnan jihar Ondo ranar asabar 26 ga watan nan.
*Kiran da bangaren PDP da Sanata Ahmed Makarfi ke jagoran ta ya yi na a dage zaben don hakan ya ba da damar kammala shari'ar dan takarar jam'iyyar da ke gaban kotun daukaka kara.
*Hukumar dai ta yi zama da masu ruwa da tsaki na zaben a babban birnin jihar Ondo, Akure.
*Kotun koli ta ba wa kotun daukaka kara ta Najeriya umurnin ci gaba da shari'ar samun sahihin dan takarar jam'iyyar PDP a zaben gwamnan Ondo.
*Tun farko babbar kotun tarayyar Najeriya ta ba wa Jimoh Ibrahim takarar wanda zuwa yanzu shi hukumar zabe ta amince da sunan sa don takarar bisa umurnin kotu.
*Dan takarar bangaren gwamna Olusegun Mimiko na Ondo wato Eyitayo Jegede na bukatar kotun ta tabbatar ma sa takarar.
*Wassu sakonni na wayar salula sun yayata wani labarai, da alamu ke nuna neman firgita jama'a ne inda su ke baiyana wai 'yan ta'addan Boko Haram sun fantsama har zuwa yankunan kudancin Najeriya.
*Sakon dai ya nuna ya fito ne daga jami'an tsaron Najeriya don ba wa jita-jitar karfin tasiri.
*Duk binciken da mu ka gudanar ya nuna labarin ba gaskiya ba ne.
*A kan samu irin wadannan sakonnin da kan nuna wa imma daga jami'an tsaro ne ko daga ofishin jakadancin Amurka a Najeriya da ke da zummar razana jama'a.
*Babbar kotun tarayyar Najeriya ta ba da belin alkalin kotun koli Jostis Ngwuta kan naira miliyan 100 wanda hukumar yaki da cin hanci da rashawa EFCC ta gurfanar da shi gaban kotun bisa tuhumar cin hanci da rashawa.
*Jostis Ngwuta da sauran alkalai 6 na fuskantar irin wannan tuhuma bayan samame da hukumar tsaron farin kaya ta kai gidajen su.
*Tuni dai alkalai su ka dakata daga jagorantar shari'u a kotuna sai bayan kammala shari'ar su da gano sun a da laifi ne koko a'a.
*Garin Aleppo a kasar Sham na ci gaba da dandana barin wuta biyo bayan kin amincewar da gwamnatin Shugaba Bashar Al-Asad ta yin a yarjejeniyar tsagaita bude wuta da majalisar dinkin duniya ke jagoranta.
*Baya ga hare-hare daga gwamnatin Asad,Kasar Rasha da kungiyar 'yan shi'a ta Hezbollah da ke Lebanon na tayawa wajen wannan yakin da hakan ya hana garin zaman lafiya.
*Rayuwa a Aleppo ba ta da tabbas don komai ya na iya faruwa koyaushe ta hanyar barin boma-bomai.
Ibrahim Baba Suleiman
Jibwis Social Media
23/Safar/1438
23/November/2016
No comments:
Post a Comment
Your Comment will help us to improve