Tuesday, 22 November 2016

LABARAI A TAKAICE


*Hukumomin Kasar Saudiya tare da hadin gwiwar hukumar mahajjatan Najeriya sun mikawa magadan Alhazai goma sha biyu na jihar Adamawa da suka rasa ransu a turairainiyar da ta abku lokacin akin hajjin 2015

*Tun a bara Hukumar Alhazan ta baiwa ko wace jiha kayan Alhazan na wadanda suka rasa rayukan su a turmutsitsin Mina, kusan dukkan jihohin da abun ya shafa sun raba nasu, illa Jihar Adamawa wanda sai a wannan karo ta samu damar rabawa 'yan uwan mamatan kayayyakin su.

*Rundunar sojin kasa a Naijeriya ta musanta cewa ta rage yawan sojojinta a Maiduguri, babban birnin jihar Borno.

*Rundunar sojin na mayar da martani ne akan fargabar da wasu mazauna birnin Maiduguri ke yi cewa, karuwar hare-haren kunar bakin wake daga 'yan kungiyar Boko Haram yasa gwiwar su ta yi sanyi.

*Hukumar ta ce tattalin arzikin ya kara samun koma baya ne da sama da kashi 2.

*Najeriya dai ta fada cikin matsalar tattalin arziki ne sakamakon faduwar farashin danyen mai a kasuwar duniya inda farashin ya yi mugunyar faduwa daga dala 100 zuwa kasa da 50.

*Barayin da suka sace Minista Bagudu Hirse sun dauka shine MAMMAN DAURA domin shi suka zo nema - Inji wanda suke tare da Minista Bagudu Hirse a lokacin da aka sace shi.

*Pukat yace Jami'an tsaron gidan Mamman Daura sun bashi kunya domin gaba dayansu sun ari na kare a lokacin da sukaji Mutanen suna harbi sama.

Ya ce wani maigadi ne ma ya zo ya rufe kofar gidan bayan sun tafi.

*Alkalumman da hukumar Kiddidiga a Najeriya ta fitar na cewa tattalin arzikin kasar ya sake samun koma baya a cikin watanni uku da suka gabata sakamakon hare-hare da ake kai wa kan bututun mai a yankin Neja Delta da kuma karanci kudaden waje a hannun 'yan kasuwa.

*Samamen da hukumar tsaron farin kaya DSS ta kai kasuwannin canjin kudi a Najeriya don tilasta saukar da farashin dala ,ya jefa tsoro a zukatan 'yan canjin.

*A kasuwar canjin ta babban birnin Najeriya Abuja Zone 4, 'yan canjin na zukewa zantawa da manema labaru don ka da allura ta tono garma.

Jibrin Zakar na daga kalilan daga 'yan canjin da ya bayyana cewa matakin da a ka dauka a kan 'yan canjin ya yi tsauri don in za a bi ta tattaunawa za a gane inda matsalar ta ke.

Ibrahim Baba Suleiman
Jibwis Social Media
22/Safar/1438
22/November/2016

No comments:

Post a Comment

Your Comment will help us to improve