Sunday, 20 November 2016

LABARAI A TAKAICE


*Kungiyar Ahlussunnah Wal Jama'a JIBWIS ta yi gagarumin taron wa'azi a Sokoto cibiyar daular Usmaniyya da ke arewa maso yammacin Najeriya.

*Wa'azin dai ya ta'allaka ne kan yaki da cin hanci da rashawa da kuma baiyana yadda daular Usmaniyya ta Shehu Usmanu Dan Fodio ta ba da gudunmawar yada Sunnah a nahiyar Afurka.

*Manyan malamai da alarammomi ne suka gabatar da kasidu tare da wa'azi a  daidai lokacin da kungiyoyin Ahlussunnah ke kara dagewa wajen cusawa al'umma sahihiyar akidar Islama da kiyaye doka da oda.

*Rundunar 'yan sandan Najeriya ta ba da labarin sake dakile harin da wani dan kunar bakin wake ya so kai wa kan sansanin 'yan gudun hijira na gidan kwastam da ke kan hanyar Gamborun Ngala a Maiduguri.

*Labarin dai ya nuna dan kunar bakin waken ya ki tsayawa a bincike shi da kan ya sanya a ka bude ma sa kuma damarar sa ta bom ta fashe ta hallaka shi.
Dan kunar bakin waken dai shi kadai ya rasa ran sa.

*Bangaren Sanata Makarfi na babbar jam'iyyar adawar Najeriya PDP na ci gaba da fatar kotu za ta musanya dan takarar jam'iyyar Jimoh Ibrahim da Eyitayo Jegede.

*Jimoh Ibrahim dai wanda babbar kotun tarayya ta ba shi takarar na bangaren jam'iyyar ne da Sanata Ali Modu Sherif ke jagoranta.

*Yanzu dai lamarin na kotun daukaka kara mako daya gabanin gudanar da zaben a ranar asabar 26 ga watan nan.

*Wassu 'yan ta'adda a yankin Dammam na Saudiyya sun hallaka wani Jami'in sojan Saudiyya.
Irin wannan kisan gilla shine na biyu a kasa da wata daya da 'yan bindigar da ba a san ko su waye ne ba su ka kai.

*'Yan sandan Saudiyya na ci gaba da binciken wannan ta'addancin.

Ibrahim Baba Suleiman
Jibwis Social Media
20/Safar/1438
20/November/2016

No comments:

Post a Comment

Your Comment will help us to improve