Saturday, 19 November 2016

LABARAI A TAKAICE


*Babban hafsan rundunar sojan kasan Najeriya Laftanar Janar Tukur Yusuf Buratai ya gana da jakadan babban sakataren majalisar dinkin duniya Muhammad Ibn Chambers a helkwatar yaki da Boko Haram a Maiduguri da ke da taken " Operation lafiya dole "

*Buratai ya ce yawancin 'yan Boko Haram da su ka yi saranda ba 'yan Najeriya ba ne.

*Buratai ya shaidawa Chambers cewa rundunar ta gano kashi 60% na 'yan ta'addan ba ma 'yan Najeriya ba ne.

*Babban hafsan ya ce rundunar ba za ta daina fafatawa ba sai ta gama da 'yan ta'addan.

*Chambers ya yi amfani da damar wajen ta'aziyya ga rundunar bisa rasuwar Laftanar Kanar Abu Ali da wassu dakaru 6 a fagen daga a Malam Fatori.

*Ofishin jakadancin Amurka a Najeriya ya nuna da abun da ya ce arangamar 'yan sanda da 'yan Shi'a a Kano da ofishin ya ce hakan ya yi sanadiyyar mutuwar rubin sha bibbiyu na 'yan an Shi'an.

*A sakon da ofishin ya aikawa gidajen labaru,ya bukaci gudanar da bincike da kira ga gwamnatin Najeriya ta ke tattaunawa da 'yan shi'an da mutunta 'yancin gudanar da ibada ta kowacce kungiya.

*Hakanan ofishin ya bukaci yin adalci kan arangamar 'yan Shi'a da rundunar sojan Najeriya a Zaria a Disambar bara.

*Ofishin dai na nuna tamkar 'yan sandan sun yi amfani da karfin da ya wuce kima kan 'yan Shi'a.

*A nasu bangaren 'yan Shi'an da shugaban Ibrahim Elzakzaky na aza alhakin akasin da ke samun su kan Amurka da Isra'ila.

*Mataimakin shugaban 'yan Shi'an Yakubu Yahaya ya ce gwamnatin Najeriya na biyewa bukatun kasashen turai ne irin Amurka wajen takurawa 'yan shi'an.

*Rundunar 'yan sandan Najeriya ta ba da tabbacin mutuwar wata 'yar kunar bakin wake daya da ta tada bom din da ke jikin ta da hakan ya kuma yi sanadiyyar mutuwar abokin tafiyar ta daya.Baya ga mutuwar 'yan kunar bakin waken biyu daf da buhunan yashin bigiren tsaron 'yan sanda, an samu nasarar damke mace daya da ran ta da a yanzu a ke gudanar da bincike.

*Rahotanni daga jihar Zamfara da ke arewacin Nigeria sun ce 'yan bindiga masu fashin shanu sun sace mutane fiye da arba'in a jihar.
A ranar Juma'a ne da dai masu fashin shanun suka sace mutanen a lokaci guda domin yin garkuwa da su.

*Akasarin mutanen da suka yi awon gaba dasu dai 'yan kasuwa ne da ke kan hanyarsu ta zuwa cin kasuwa daga kauyukansu.

*Wata tankar man fetur ta fadi a kasar Muzambik inda ta kama da gobara da hakan ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 73 fiye da 100 su ka samu raunuka.

*Mutanen dai sun gamu da akasin ne a yayin da su ke kamfatar man da ke malala daga motar wacce daga bisani ta kama da wuta.
Lamarin ya auku ne a yankin Tete da ke kan iyakar Muzambik da Malawi.

Ibrahim Baba Suleiman
Jibwis Social Media
19/Safar/1438
19/November/2016

No comments:

Post a Comment

Your Comment will help us to improve