Thursday, 22 June 2017

KWAMITIN TALLAFAWA MARAYU, SUN TALLAFAWA MARAYU,1,252.00 YAU A BIRNINKEBBI


A yaune  kwamitin tallafawa marayu da ke masallacin *jibwis* na sheikh *Abbas jega* dake  anguwar rafin atiku  a nan cikin garin Birninkebbi suka  tallafawa marayu dubu daya da  dari biyu da hamsin da biyu (1,252.00) a wuraren da  suka  tsara  a nan  cikin garin Birninkebbi,
Shugaban kwamitin Alhaji *Abdullahi Gebe*  ne  ya  sanar da  hakan  a lokacin da  manema labarai  suka ziyarci  wurin da  ake  bayar da  tallafin  da  safiyar yau,

Haka shima Uban Doman Gwandu  Alhaji  *Khalidu Sa'ad,*  yayi kira  ga  gwamnati, yan kasuwa,  yan siyasa da kuma  Ma'aikata  da  su  bada  goyon bayan su  ga  wannan shirin  da  kungiyar izala ta  kasa  ta  kirkiro  tun  shekaru  da  suka gabata  domin  tallafin  yanada  alfano  matuka,

Anashi  bayanin  daga  bisani,shugaban kwamitin,  Alhaji *Abdullahi  Gebe  Argungu*  ya  yi  matukar godiya  amadadin kwamitin baki daya, ga  duk ilahirin  wadanda suka bada nasu tallafin  domin wannan shirin ya ci nassara, Musamman shugaban masu rinjaye  a majalisar jaha  watau  Hon. *Bello  Rilisco* akan bada tallafi mafi tsoka  a kowace  shekara,
Allah ya sa ka wa  kowa da alkhairi,

*Adamu Attahiru*
Jibwis social media
26/09/1438
21/06/2017

No comments:

Post a Comment

Your Comment will help us to improve