Thursday, 29 December 2016

LABARAI A TAKAICE

LABARAI A TAKAICE

*Rundunar sojan Najeriya ta ce ta samu KOFIN ALKUR'ANUL KARIM da shugaban 'yan ta'addan Boko Haram Abubakar Shekau ke rikewa da kuma tutar helkwatar sa a dajin Sambisa da a ka ragargaza.

*Rundunar ta ce ta hakikance littafin mai girma mallakar Shekau ne da ya bari lokacin da ya arce.

*Yanzu dai za a mika KOFIN NA ALKUR'ANUL KARIM ga babban hafsan rundunar sojan Najeriya Laftanar Janar Tukur Buratai don ya mika shi ga shugaba Buhari.

*Daga wannan labari dai za a fahimci Abubakar Shekau ka iya zama ya arce ne ba ya rasa ran sa daga lugudan wuta ta sama ba.

*Ministan tsaron Najeriya Burgediya Janar Mansur Dan Ali ya ce tun 'yan makwanni sojoji ke tsare-tsaren murkushe 'yan ta'adda a dajin Sambisa inda da zarar kammala ruwan damuna a ka samu sararin jefa boma-bomai kan maboyar 'yan ta'addan a dajin.

*Dan Ali ya kara da cewa bayan kammala jefa boma-boman dakarun sojan kasa sun shiga dajin inda su ka kammala share fage da kwace dajin.

*Hakanan ministan ya ce ta kan yi wu sauran matan Chibok sun saje cikin kimanin mutum 1000 da a ka ceto daga dajin kuma ba mamaki sun yi aure da sai an tantance za a gano su.

*Ministan ya yi kira ga mutane su ci gaba da taka tsantsan da mutanen da ba su gane take-taken su ba da kai irin wannan labari ga jami'an tsaro.

*Jami'an soja sun tabbatar da damke wani dan Boko Haram da alamu su ka nuna ya arce ne daga dajin Sambisa inda ya shigo anguwar Utako Abuja ya fara wa'azi rike da Alkur'ani mai girma da kuma sarka a wuyan sa mai alamar gicciye na Yesu Kiristi.

*Masu ibada a masallacin kasuwar gwarawa da ke Jabi su ka ankara da yanayin mai wa'azin da kazalika ya ke rike da wata leda da ke da dabino da wani turare.

*Don kara bincike,an kawo wanda a ke tuhumar masallacin jumma'ar Umar Ben Khaddab inda ya rika bayanai na rashin kan gado da alamun rashin gaskiya.

*Jami'an sintiri na birnin Abuja sun gaiyato sojoji daga barikin Gowon wadanda su ka garzayo su ka yi awun gaba da shi.

*Tsohon gwamnan Kano Ibrahim Shekarau ya ce a matsayinshi na Malami har yanzu bai ga wani abin a zo a gani ba da BUHARI ya yi wa kasa Najeriya.

*Shekarau ya ce dukka abubuwan da Buhari ya ce zai yi a lokacin Kamfen har yanzu bai yi wani guda daya ba wanda za'a ce yau gashi yayi.

*Kamar Yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito tace tsohon gwamnan ya fadi hakanne a garin Gombe.

Ibrahim Baba Suleiman
Jibwis Social Media
29/Rabi-Al'Awwal/1438
29/December/2016

Albany Dabai,
08069123479.

No comments:

Post a Comment

Your Comment will help us to improve